Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Yamai ya ce ’yan sanda suka fara binciken wanda aka fara kan wani yunƙurin kashe mutane a wata unguwa da ke wajen birnin Yamai, wanda ya kai ga kama wanda ake zargi da aikata laifin.
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Yamai a yayin wani taron manema labarai a ranar Lahadi ya bayyana cewa an kama tsohon minista Ibrahim Yacoubou bisa zarginsa da kashe mutane domin yin tsafi da su.
A cewar Maazou Oumarou, komai ya fara ne daga binciken ’yan sanda wanda aka fara a ranar 29 ga Yulin 2025, kan wani yunƙurin kisa a wata unguwa da ke wajen birnin Yamai, wanda ya kai ga kama wanda ake zargi da aikata laifin a Dosso.
Wani Mahamadou Noura ne ya bayyana wa ’yan sanda cewa shi ne ya aikata wannan laifi da kuma wasu kashe-kashe guda shida “don yin tsafi da su a madadin Issa Ali Maiga da ubangidansa Ibrahim Yacoubou, Ismael Morou Karama, Elhadji Bilya da Issa Seybou Hama.”
Bayan an kama duk waɗannan mutane, “lauyan gwamnati, bayan ya tantance abubuwan da ke ciki, ya ga cewa ya zama dole a bar ’yan sandan shari’a su ci gaba da bincikensu tare da ɗaukar wasu ƙarin matakai da za su iya taimakawa wajen samun cikakken bayani game da gaskiyar al’amura, kafin ɗaukar wani mataki na gaba,” in ji sanarwar Babban Lauya na Kotun Ɗaukaka Ƙara.
Manufar “wannan umarnin na shari’a,” a cewar Babban Lauya, “ita ce a samar da cikakken rahoto wanda ya haɗa da dukkan yanayi, sannan a mika shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
A cewar mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati, ganin tsananin wannan al’amari, “ya zama wajibi a gudanar da binciken cikin gaggawa matuƙa.” Haka kuma, bayan ya tabbatar cewa za a fayyace dukkan gaskiya game da wannan shari’a, ya yi kira ga ’yan ƙasa da su mutunta ’yancin kotu kuma su ba ta cikakken amincewa.
