Wasu ‘yan bindiga sun kai hari dakunan kwanan dalibai na Kwalejin Ilimi ta Tarayya (Federal College of Education) da ke Kaura Namoda a Jihar Zamfara, inda suka yi garkuwa da dalibai bakwai.
Wani dalibin makarantar, Ibrahim Ahmad, ya bayyana cewa daya daga cikin daliban da aka sace ya samu nasarar tserewa daga hannun maharan. A cewarsa, har yanzu dalibai shida ne ke hannun ‘yan bindigar, wadanda suka hada da maza uku da mata uku.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya ce harin ya faru ne a daren Litinin lokacin da ‘yan bindigar suka zo yankin suka tarar da daya daga cikin gidajen kwanan daliban a bude.
Ya ce binciken farko ya nuna cewa wani dalibi ne ya fita daga dakin domin samun iska, inda ya bar kofar a bude ba tare da ya lura ba, lamarin da ya bai wa ‘yan bindigar damar shiga gidan tare da yin garkuwa da daliban.
DSP Yazid Abubakar ya kara da cewa rundunar ‘yan sandan jihar, musamman sashen yaki da masu garkuwa da mutane (VCRU), tare da hadin gwiwar dakarun Operation Fansan Yamma, sun kaddamar da wani samame na musamman domin ceto daliban da aka sace da kuma kamo wadanda suka aikata wannan laifi.
Ya tabbatar da cewa jami’an tsaro na ci gaba da gudanar da bincike da kuma aikin ceto domin ganin an kubutar da daliban cikin gaggawa.
